Rahotannin ya nuna cewa bayan harin da aka kai ofishin jaridar Charlie Hebdo a ranar laraba 7 a wata a birnin Paris na Faransa, an samu wassu hare-haren a wannan daren har zuwa safiyar alhamis din nan 8 ga wata a wasu wuraren ibada na Musulmai da wurare dake dab da su a kasar, sai dai babu wanda ya ji rauni ko rasa ransa. (Amina)