in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin kasashen Faransa da Jamus da Ukraine sun yi kira da a tsagaita bude wuta a gabashin Ukraine
2015-02-02 16:44:18 cri
A jiya Lahadi ne fadar gwamnatin kasar Faransa ta sanar da cewa, shugaban kasar ta Faransa Francois Hollande, da shugabar gwamnatin kasar Jamus Angela Merkel, da shugaban kasar Ukraine Petro Poroshenko sun zanta ta wayar tarho har na tsawon mintuna 45 a wannan rana, inda suka yi kira da a tsagaita bude wuta nan da nan a gabashin kasar Ukraine.

Ban da haka kuma a cewar Leonid Kuchma, tsohon shugaban kasar Ukraine, tawagar bangarori 3 masu ruwa da tsaki kan batun Ukraine da wakilan dakarun dake gabashin kasar sun yi taro don tattauna yadda za a aiwatar da yarjejeniyar Minsk a ranar 31 ga watan Janairun da ya wuce. Sai dai dalilan da suka sa ba a cimma daidaito ba a taron su ne, da farko, shugabannin da ke wakiltar gabashin Ukraine Alexander Zakharchenko da Igor Plotnitsky, wadanda suka sa hannu kan yarjejeniyar Minsk, ba su halarci taron ba. Sa'an nan na biyu shi ne wakilan dakarun da suka halarci taron sun gabatar da bukatunsu da wa'adi na karshe, kuma sun ki tattauna shirin tsagaita bude wuta da janye manyan makamai. (Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China