in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaba Hollande ya sanar da kawo karshen rudanin diplomasiyya tsakanin Faransa da Morroco
2015-09-21 10:38:23 cri
Da yake ziyarar aiki ta kwanaki biyu a kasar Morroco, shugaban kasar Faransa Francois Hollande ya tabbatar a ranar Asabar a Tanger dake arewacin Morroco, da kawo karshen rudanin diplomasiyya na kusan shekara daya da batun gabatar da wasu kararraki a kasar Faransa na cin zafarin dan adam dake shafar shugaban hukumar leken asiri ta Morroco, Abdellatif Hammouchi, da a cewarsa yanzu wannan matsala ta kare.

Ya bayyana fatansa na ganin kasashen biyu sun shiga cikin wani sabon mataki na huldar dangantaka.

Dangantaka tsakanin Faransa da Morroco za ta kasance a sahun gaba a yayin babban taro kan yanayi (COP21) da zai gudana a cikin watan Disamban mai zuwa a birnin Paris da taron COP22 da zai gudana a birnin Marrakech a shekarar 2016, in ji shugaba Hollande, tare da bayyana cewa wannan ziyara za ta kasance wata babbar dama wajen yin kira a Tanger domin ganin mun cimma nasara a yayin babban taro kan yanayi da kuma himmatuwa wajen ganin duniyarmu ta dauki matakan da suka wajaba domin tabbatar da makomarmu mai kyau.

A cikin wata sanarwar da aka fitar a albarkacin wannan ziyara, fadar shugaban kasar Faransa ta nuna cewa kasar Morroco muhimmiyar kasa ce wajen janyo hankalin nahiyar Afrika domin shirya manyan tarukan duniya kan yanayi COP21 da COP22. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China