in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Gabon zai halarci wani babban jerin gwano a Paris
2015-01-11 16:18:57 cri
Shugaban kasar Gabon Ali Bongo Ondimba ya bar Libreville a ranar Asabar zuwa birnin Paris na kasar Faransa inda zai halarci a ranar Lahadi a wani babban macin masu kishin kasa domin yin allawadai da ta'addanci, a cewar fadar shugaban kasar Gabon.

Bisa goron gyayyatar shugaban kasar Faransa, Francois Hollande, shugaba Ali Bongo Ondimba zai halarci wannan babban macin da za'a shirya a ranar yau Lahadi a birnin Paris domin nuna jimami ga wadanda suka mutu a harin da aka kai a cibiyar mujallar Charlie Hebdo da ya yi sanadiyyar mutuwar mutane goma sha biyu a ranar Laraba da safe, in ji sanarwar.

Shugaban kasar Faransa, Francois Hollande, shi ma zai halarci jerin gwanon, ya kuma gyayyaci shugaban kasashen tarayyar Turai kamar su faraministan kasar Spaniya Mariano Rajoy, shugaban kwamitin dattawan Italiya Matteo Renzi, shugabar gwamnatin Jamus Angela Merkel, faraministan Ingila David Cameron, faraministan Belgium Charles Michel, shugaban kwamitin tarayyar Turai Jean-Claude Juncker da shugaban kwamitin dattawan tarayyar Turai Donald Tusk.

A ranar 7 ga watan Janairu ne, Cherif da uwansa Said Kouachi suka kai hari a cibiyar mujallar Charlie Hebdo na kasar Faransa, tare da kashe mutane goma sha biyu da suka hada da shugabannin mujallar. Haka kuma wasu tagwayen hare-hare sun biyo bayan wannan hari na Charlie Hebdo a ranakun 8 da 9 ga watan Janairu a birnin Paris. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China