Babban magatakardan MDD Mista Ban Ki-Moon ta bakin kakakinsa ya ba da wata sanarwa a ran 4 ga wata, inda da kakkausar murya ya yi alla wadai da harin da aka kai a birnin Kudus a ran 3 ga wata, kuma ya yi kira ga shugabannin Isra'ila da Palesdinu da su yi hakuri da juna, kuma su kaucewa tsananta halin da ake ciki a halin yanzu.
Shugaban Palestinu Mahmoud Abbas ya kira mista Ban ta wayar tarho, inda ya nemi MDD da ta ba da tabbacin tsaro ga Palestinawa tun da wuri. A sa'i daya kuma, saboda ganin an kai jerin hare-hare kan 'yan Isra'ila a birnin Kudus, 'yan sanda Isra'ila sun sanar da wani mataki a wannan rana cewa, ban da mazauna wurin, 'yan kasuwa, dalibai, masu yawan shakatawa da 'yan Isra'la, ba wanda zai iya shiga Kudus a wadannan kwanaki biyu ba. (Amina)