in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin babban sakataren MDD ya kalubalanci Palesdinu da Isra'ila da su gudanar da shawarwari cikin lumana nan da nan
2014-10-30 15:46:50 cri
Mataimakin babban sakataren MDD mai kula da harkokin siyasa Jeffrey Feltman, ya ce shirin gina sabbin matsugunan yahudawa da Isra'ila ta tsara aiwatarwa a birnin Kudus, na tsananta halin da ake ciki tsakanin Palesdinu da Isra'ila. Kana ya yi kira ga bangarorin biyu da su sake rungumar shawarwari cikin lumana ba kuma tare da bata wani lokaci ba.

Feltman ya bayyana hakan ne a gun taron da kwamatin sulhu na MDD ya gudanar kan batun yankin gabas ta tsakiya, biyowa bayan rahotannin dake cewa Isra'ila ta amince da shirin gina sabbin matsugunai fiye da 1000 a gabashin birnin Kudus, matakin da kuma ya tada hankalin babban sakataren MDD Ban Ki-moon.

An dai yi hasashen cewa, aiwatar da wannan shiri, zai kawo illa ga yarjejeniyoyin da Palesdinu da Isra'ila suka cimma kan shimfida zaman lafiya. Kaza lika gina matsugunan ya sabawa dokokin kasa da kasa, da ma shirin da bangarorin biyu suka tsara game da hakan. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China