in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ya kamata shugaban Palesdinu ya dauki alhakin harin da aka kai ga birnin Kudus, a cewar firaministan Isra'ila
2014-11-06 16:08:04 cri

Firaministan kasar Isra'ila Benjamin Netanyahu ya bayyana a ranar 5 ga wata cewa, ya kamata shugaban Palesdinu Mahmoud Abbas ya dauki alhakin harin da aka kai ga birnin Kudus a wannan rana.

Netanyahu ya yi jawabi a gun bikin cika shekaru 19 da kisan tsohon firaministan kasar Yitzhak Rabin cewa, an kai hari ga birnin Kudus a tsakar ranar 5 ga wata bisa zugawar shugaba Abbas da kungiyar Hamas suka yi wa jama'arsu domin su aikata hakan.

A ranar 5 ga wata a birnin Kudus, an kara samun hare haren da Palesdinawa suka kai wa 'yan sanda da fararen hula a dab da hanyar jiragen kasa, wanda ya haddasa mutuwar dan sanda daya, yayin da mutane fiye da 10 suka ji rauni. Bayan abkuwar lamarin, kungiyar Hamas ta sanar da daukar alhakin kai harin a cikin sanarwarta. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China