in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Majalisar dokokin kasar Faransa ta jefa kuri'ar neman amincewar Palesdinu ta kasance mai cin gashin kanta
2014-12-03 15:32:12 cri
Majalissar dokokin kasar Faransa ta amincewa da Palesdinu a matsayin kasa mai cin gashin kanta, bayan kada kuri'un goyon baya game da hakan. Sakamakon da aka bayyana dai ya nuna amincewa da kudurin da kuri'u 339, adadin da ya yi matukar haura na masu adawa, wadanda suka samu kuri'u 151.

Bisa hakan ne kuma majalisar dokokin kasar ta yi kira ga gwamnatin kasar Faransa, da ta amince Palesdinu a matsayin kasa mai 'yanci, tare da fatan za a warware matsalolin Palesdinu ta hanyar amince da ita.

A wannan rana, ministan harkokin wajen Palesdinu Riyad al-Malki ya bayyana cewa, kudurin na majalisar dokokin kasar Faransa zai sa kaimi, ga amincewa da Palesdinu a nahiyar Turai.

Kafofin watsa labaru na kasar Faransa sun tsamo sanarwar da ofishin jakadancin Isra'ila dake kasar Faransa ya fitar, wadda ke cewa kudurin zai jinkirta cimma yarjejeniyar shimfida zaman lafiya tsakanin Palesdinu da Isra'ila.

Ana dai kallon amincewar da Palesdinu ta samu a majalisar dokokin kasar Faransa a matsayin batu mai matukar ma'ana, koda yake hakan na bukatar amincewar shugaban kasar François Hollande, wanda zai bayyana matsayin karshe kan wannan batu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China