in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Palasdinawa ya sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyin kasa da kasa
2015-01-01 15:55:50 cri
Shugaban Palasdinawa Mahmoud Abbas ya sanya hannu kan wasu yarjejeniyoyi guda 20 da kuma shiga wasu hukomomi, ciki har da kotun hukunta manya laifuffuka ta kasa da kasa (ICC), bayan da kwamitin sulhu na MDD ya ki amincewa da wani daftarin kuduri da aka gabatar da nufin kawo karshen mamayar da Isra'ila ke yiwa yankunan Palasdinawa.

Shugaba Abbas ya bayyana hakan ne bayan sa hannun shiga wadannan hukumomi da kulla yarjejeniyoyi yayin da yake jagorantar wani taron shugabannin kwamitin kungiyar PLO a birnin Ramallah.

Abbas ya ce, Palasdinawa na da 'yancin shiga duk wata hukuma ko kulla wata yarjejeniya da nufin kafa kasar Palasdinu bisa tsarin kan iyaka da Isra'ila ta mamaye a shekara ta 1967 mai hedkwata a gabashin birnin Kudus kamar yadda dokokin kasa da kasa suka tanada.

Ya kuma bayyana rashin jin dadinsa kan yadda kudurin ya gaza samun amincewar kuri'un da ake bukata a kwamitin sulhu na MDD. Sai dai ya yi fatan samun kuri'u 9 da ake bukata a nan gaba.

Ya kuma bayyana kudurinsa na gurfanar da kasar Isra'ila a gaban kotun na ICC kan yadda take kai hare-hare kan Palasdinawa tare da kwace masu filaye a kowa ce rana.

Shugana Abbas ya ce, hanya daya tilo ta kawo karshen rikicin yankin baki ita ce magance rikicin Palasdinu da Isra'ila . (Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China