in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasashen duniya sun nuna goyon baya ga Palesdinu a babban taron MDD
2014-09-30 15:35:07 cri
A yau aka shiga kwana na shida na babbar muhawara a babban taron MDD karo na 69, inda ya zuwa yanzu shugabannin kasashe da gwamnatocin kasashe fiye da dari daya suka yi jawabi. Wakilan kasashe da dama sun yi amfani da wannan damar tattauna batutuwan duniya, don bayyana ra'ayoyinsu na nuna goyon baya ga al'ummar Palesdinu.

Ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya bayyana cewa, kasar Sin tana kira ga Isra'ila da Palesdinu da su cimma yarjejeniyar tsagaita bude wuta na dogon lokaci. Sannan bai kamata a ci gaba da jinkirtar bukatun al'ummar Palesdinu na neman kafa kasarsu ba.

Shi kuwa mataimakin firaministan kasar Syria kuma ministan harkokin wajen kasar Walid Muallem ya bayyana cewa, bai kamata a yi watsi da ikon jama'ar Palesdinu na komawa gidajensu da zabar makomar kasarsu da kansu ba.

Shugaban kasar Qatar Sheikh Tamim Bin Hamad al Thani ya yi kashedi cewa, yin amfani da karfin tuwo ba zai kawo karshen turjiyar da al'ummar Palesdinu ke nuna wa ba, sannan za a samar da tsaro ga jama'ar Isra'ila ne kawai ta hanyar lumana. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China