in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta kalubalanci Isra'ila game da dakatar da gina matsugunan yahudawa
2014-10-30 15:50:09 cri
Zaunannen wakilin Sin a MDD Liu Jieyi ya ce Sin na kira ga Isra'ila da ta dakatar da gina matsugunan yahudawa ba tare da bata lokaci ba, domin magance tsanantar halin da ake ciki, da kuma samar da yanayi da zai bada damar fahimtar juna tsakanin sassan biyu, tare da ci gaban shawarwari cikinsu.

Mr. Liu wanda ya bayyana hakan a cibiyar MDD dake birnin New York, yayin zaman kwamitin sulhu na MDD game da yankin gabas ta tsakiya, ya kara da cewa batun gina matsugunan yahudawa na daya daga cikin muhimman ayyukan dake kawo cikas ga wanzar da yanayin zaman lafiya a yankin gabas ta tsakiya. Kana gudanar da shawarwari ne kadai hanya daya tilo wajen wanzar da zaman lafiya tsakanin Palesdinu da Isra'ila.

Ya ce kasar Sin na goyon baya ga bukatu, da hakkin jama'ar Palesdinu, game da kafa kasarsu mai cin gashin kanta, kuma za ta ci gaba da kokari tare da sauran kasashen duniya wajen sa kaimi ga samun zaman lafiya a daukacin yankin gabas ta tsakiya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China