in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wakilin Sin ya kalubalanci Palesdinu da Isra'ila da su gaggauta komawa teburin shawarwari
2015-04-22 11:02:18 cri
Mataimakin zaunannen wakilin Sin dake MDD Wang Min, ya kalubalanci Palesdinu da Isra'ila da su gaggauta komawa teburin shawarwari domin cikin yanayin zaman lafiya da lumana.

Wang Min ya bayyana hakan ne a jiya Talata, yayin muhawarar da kwamitin sulhun MDD ya gudanar, game da batun yankin gabas ta tsakiya. Ya ce warware matsalar Palesdinu da Isra'ila na da matukar muhimmanci, duba da halin rashin kwanciyar hankali da ake fama da shi yanzu haka a yankunan gabas ta tsakiya.

Wang Min ya ce, kamata ya yi Palesdinu da Isra'ila su tsaya tsayin daka wajen aiwatar da shawarwari cikin lumana. Duba da cewa shawarwarin ne kadai za su iya samar da hanyar warware matsalar bangarorin biyu, da ma batun kafuwar kasar Palesdinu, da kuma dauwwamar zaman tare cikin lumana tsakanin bangarorin biyu.

Ya ce kasar Sin na fatan bangarorin biyu za su cimma daidaito, da bin hanyar shimfida zaman lafiya, da komawa shawarwari cikin hanzari. Kana Sin na da burin ganin bangarorin biyu sun kai ga amincewar juna, da dakatar da gina matsugunai, da kawar da shinge da aka kafa a zirin Gaza. Hakazalika kuma, ya kamata a dora muhimmanci sosai ga abubuwan da kasar Isra'ila take baiwa kulawa. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China