Babban magatakardan MDD Mista Ban Ki-Moon ya nuna bakin cikinsa sosai kan mutuwar masu kiyaye zaman lafiya na MDD 'yan asilin kasar Ruwanda a kasar Afrika ta tsakiya a jiya Asaba ran 8 ga wata, tare da bayyana takaici da juyayi ga iyalan mamatan, da gwamnatin kasar Ruwanda da jama'arta.
Mista Ban kuma ya kara da cewa, ana kokarin bincike kan gano dalilin abkuwar wannan lamarin da ya yi sanadin mutuwar masu wanzar da zaman lafiya biyar na MDD, yayin da wasu 8 suka ji raunuka, ba tare da daba wani karin haske ba kan lamarin. (Amina)