in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Magatakardan MDD ya yi matukar mamakin harin da aka kai ma ma'aikatan wanzar da zaman lafiya a CAR
2014-10-10 14:23:14 cri

A ranar Alhamis din nan 9 ga wata, babban magatakardan MDD Ban Ki-Moon ya bayyana matukar mamakinsa game da harin da aka kai ma ma'aikatan wanzar da zaman lafiya a birnin Bangui na kasar Jamhuriyar Afrika ta Tsakiya a safiyar wannan rana, abin da ya yi sanadiyyar mutuwar mutum daya da jikkata wadansu guda 8.

Wadansu mutane ne da ba a sansu ba suka kai wannan mummunan harin a kan ayarin ma'aikatan wanzar da zaman lafiya a Bangui kamar yadda wata sanarwar da kakakin majalissar ya fitar ma manema labarai.

Wannan a cewar sanarwar shi ne karo na farko da ma'aikacin wanzar da zaman lafiya ya halaka a kasar tun karbar da ikon tafiyar da aikin daga hannun kungiyar wanzar da zaman lafiya dake karkashin tarayyar kasashen Afrika a ranar 15 ga watan satumbar bana.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China