in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sojoji biyu sun mutu sakamakon harin da aka kai a Mali
2015-08-03 10:44:13 cri
Gwamnatin kasar Mali ta ce sojojin kasar su 2 sun rasa rayukan su, wasu kuma da dama sun jikkata sakamakon wani hari da aka kaddamar kan wata rundunar soja dake kan wata babbar hanyar mota a jihar Ségou dake tsakiyar kasar Mali.

Sanarwar ta ce, lamarin ya auku ne da misali karfe 3 na yammacin ranar Asabar, lokacin da sojojin kasar ke fafarar wasu masu laifi, tare da kwace wasu makamai daga hannunsu. Koda yake ba a yi cikakken bayanin asalin su ba tukuna.

Sanarwar da gwamnatin ta bayar, ta kuma yi kakkausar suka game da harin wanda aka bayyana da danyen aikin rashin imani. A cewar sanarwar irin wannan aiki zai kawo cikas ga kokarin da ake yi na shimfida zaman lafiya a kasar.

Rahotanni na nuna karuwar hare-hare a arewacin kasar Mali. Duk kuwa da cewa gwamnatin kasar ta daddale yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya da wakilan wasu daga dankarun dake birnin Bamako fadar mulkin kasar, da na arewacin kasar a ranar 15 ga watan Mayun da ya shude. Sai dai koda a wancan lokaci manyan sassa uku na kungiyar CMA ba su sa hannu kan yarjejeniyar tsagaita wutar ba.

A kuma ranar 20 ga watan Yuni, CMA ta rattaba hannu kan wannan yarjejeniyar, matakin da ya alamanta cewa daukacin bangarori dake da nasaba da lamarin sun amince da wannan yarjejeniya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China