in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mali ta damke wasu mutane 20 da ake zargin 'yan ta'adda ne
2015-07-15 19:07:13 cri
Mahukuntan kasar Mali sun ce sun cafke wasu mutane 20, ciki hadda 'yan kasar Faransa su biyu, wadanda ake zargin 'yan ta'adda ne a garin Zegoua, mai iyaka da kasar Cote d'Ivoire.

Wata majiya ta shaidawa kamafanin dillancin labarum kasar Sin Xinhua cewa, cikin wadanda aka kame hadda 'yan kasar ta Mali, da 'yan Mauritania. An kuma ce sun tsallaka cikin kasar ne daga Cote d'Ivoire a ranar Litinin. Tuni dai aka garzaya da su zuwa babban birnin kasar Bamako.

Wannan dai lamari na zuwa ne 'yan kwanaki, bayan da jami'an tsaron kasar suka cafke wasu 'yan ta'addar na daban, cikin su hadda daya dauke da takardun farfaganda, na kungiyar Ansar Dine ta masu Jihadi, kungiyar da a baya bayan nan ta dauki alhakin kai hare-hare kan rundunar sojojin kasar, da dakarun tawagar wanzar da zaman lafiya dake kasar, a yankunan arewaci da kuma kudancin kasar.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China