in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta bukaci a tsagaita wude wuta a arewacin Mali
2015-05-02 17:04:40 cri
Kwamitin sulhu na MDD ya fidda wata sanarwa a jiya Juma'an, inda ya nuna matukar damuwa, dangane da tashe-tashen hankula da suke wakana a arewacin kasar Mali, kuma ya bukaci bangarorin da abin ya shafa da su tsagaita bude wuta ba tare da bata lokaci ba, tare da gaggauta samar da daftari na yarjejeniyar wanzar da zaman lafiya.

Cikin sanarwar, kwamitin ya kuma bayyana cewa barkewar rikice-rikice a yankin Gao dake arewacin kasar ta Mali, tun daga ranar 27 ga watan Afrilun da ya gabata, ya sabawa yarjejeniyar tsagaita bude wuta da aka sanyawa hannu a baya.

Kana kwamitin sulhu ya nuna goyon baya ga matakan da sojojin kiyaye zaman lafiya na MDD ke dauka, don sassauta yanayin da ake fuskanta a kasar ta Mali, da kuma kokarinsu, wajen ciyar da shawarwari tsakanin bangarorin daban daban gaba. Bugu da kari, kwamitin na sa kaimi ga bangarorin daban daban na kasar da su ci gaba da halartar zaman shawarwari, domin cimma nasarar kulla daftari na yarjejeniyar zaman lafiya a birnin Bamako, fadar mulkin kasar, wanda ake sa ran gudanar a ranar 15 ga watan nan na Mayu. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China