in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rantsar da sojojin kiyaye zaman lafiya rukuni na uku da Sin za ta tura zuwa Mali
2015-05-12 20:05:49 cri
A yau Talata ne a garin Teku dake lardin Liaoning na kasar rudunar sojan kasar Sin ta yi bikin rantsar da rukuni na uku na sojojin kiyaye zaman lafiya da kasar Sin za ta tura zuwa kasar Mali, domin gudanar da aikin kiyaye zaman lafiya a kasar na tsawon watanni takwas.

Rahotanni na cewa, tawagar sojojin tana kunshe ne da mutane guda 395, wadanda suka hada da kananan tawagogi guda uku na 'yan sanda, sojojin injiniya da na ba da jinya, wadanda aka tura zuwa yankin Gao na kasar Mali.

Bugu da kari, gabanin su fara wannan aiki na kiyaye zaman lafiya, wadannan kanannan tawagogi guda uku suka fara samun horo a asirce, sa'an nan kuma, sojojin za su kara fahimtar dokoki, al'adu da kuma harkokin addinin kasar Mali, wannan zai taimaka musu wajen tabbatar da kammala ayyukansu cikin nasara. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China