in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kungiyar Nasar ta dauki alhakin kai hari a arewacin Mali
2015-04-18 17:16:38 cri
Kungiyar ta'addanci ta Nasar ta fitar da wani labari a ran 17 ga wata, inda ta sanar da daukar alhakin kai wani harin kunar bakin wake a yankin Gao dake arewacin kasar Mali a kwanan baya.

Kungiyar ta fitar, an ce, babban makasudin harin din da kungiyar ta shirya shi ne kai farmaki ga rundunar sojan kasar Nijer ta tawagar sulhu ta musamman da MDD ta tura zuwa kasar Mali, kana kungiyar ta shirya harin domin nuna kiyayya ga kasashen Faransa da Amurka da su kafa sansanonin soja a kasar Mali, da kuma halartar shugaban kasar Nijer taron gangami kan mujallar Charlie domin nuna goyon baya ga kasar Faransa.

A ran 15 ga wata, wata mota dake daukar boma-bomai ta shiga sansanin tawagar sulhu ta musamman ta MDD a garin Ansongo dake yankin Gao, inda boma boman suka tashi, lamarin da ya haddasa mutuwar fararen hula guda uku, yayin da 16 suka jikkata, ciki har da da sojojin kiyaye zaman lafiyar kasar Nijer guda 9. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China