in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta damu game da hare-hare kan jami'an wanzar da zaman lafiya a Mali
2015-04-25 17:28:58 cri
Babban magatakardar MDD Ban Ki-moon, ya bayyana matukar damuwa game da yawaitar hare-hare kan jami'an wanzar da zaman lafiya a kasar Mali.

Mr. Ban wanda ya bayyana hakan ta bakin kakakin MDD Stephane Dujarric, ya ce ya zama wajibi a dauki matakan warware matsalar Arewacin kasar ta Mali bisa dabaru na siyasa. Wannan dai tsokaci na Ban Ki Moon na zuwa ne kwanaki 2, bayan aukuwar wani hari da ya raunata wasu jami'an tawagar MINUSMA su 7, sakamakon wata nakiya da motar da suke ciki ta taka a yankin Kidal.

Daga makon da ya gabata zuwa yanzu, hare-haren da ake shiryawa a wannan yanki sun yi sanadiyar rasuwar fararen hula 5, da jikkatar wasu 13, baya ga jami'an wanzar da zaman lafiyar MDDr su 16 da hare-haren suka raunata.

Kwamitin tsaron MDD ne dai ya kafa tawagar MINUSMA cikin shekarar 2013, tawagar da aka dorawa alhakin tallafawa shirin dawo da tsarin dimokaradiyya a kasar, tare kuma da baiwa harkokin tsaro tallafin da ya wajaba.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China