Sanarwar kuma ta yi kira ga shugabannin kasar da mabiyansu, da su warware matsalolin da ka iya bullowa yayin zaben bisa tsarin mulkin kasar. Ban da haka Ban Ki-Moon ya nanata cewa, MDD na goyon bayan aikin share fagen gudanar zaben, da kuma kokarin da jama'ar kasar ke yi na kiyaye dimokuradiyyar kasar. (Amina)