in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kafa sabuwar gwamnati a kasar Togo
2013-09-18 16:15:12 cri
A ranar 17 ga wata da dare ne, aka kafa sabuwar gwamnati a kasar Togo karkashin shugabancin firaministan kasar Kwesi Seleagodji Ahoomey- Zunu. A wannan rana da dare, babban sakataren fadar shugaban kasar Togo ya karanta umurnin shugaban kasar Faure Essozimna Gnassingbe game da sunayen da ke cikin sabuwar gwamnati ta gidan talebijin din kasar.

Sabuwar gwamnatin na kunshe da mambobi 27, cikinsu,har da tsohon mai ba da shawara ga shugaban Faure ta fuskar diplomasiyya Robert Diesel wanda ya zama ministan harkokin wajen kasar, yayin da wani tsohon mai ba da shawara ga shugaban ta fuskar diplomasiyya na daban Kofi Esaw ya rike mukamin ministan shari'a da hukumomin kasar. Haka kuma, tsohon ministan harkokin wajen kasar Elliott OHIN ya zama ministan kula da tsare-tsaren samun ci gaba.

A ranar 25 ga watan Yuli na bana ne, aka yi zaben majalisar dokoki a kasar Togo,inda jam'iyyar hadin gwiwa don kiyaye jamhuriyar Togo da ke karkashin shugabancin Faure, ta samu kujeru 62 cikin kujeru 91 a majalisar dokokin kasar. A ranar 6 ga wata, Faure ya ba da umurnin sake nada Ahoomey-Zunu a matsayin firaministan kasar, kuma ya bukace shi da ya kafa sabuwar gwamnati.(Bako)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China