Taron ministoci na ranar Jumma'a ya dauki wannan mataki ta yin la'akari da bukatun da shugaban kungiyar ci gaban tattalin kasashen yammacin Afrika ECOWAS mai ci yanzu wato shugaban kasar Ghana John Hahama Dramani ya gabatar a karshen wata ziyarar aiki a ranar 24 ga watan Maris, a yayin shawarwarin da ya yi tare da hukumomin kasar Togo, 'yan takarar zaben shugaban kasa da kuma hukumar zabe mai zaman kanta ta CENI, a cewar wata sanarwa da gwamnatin kasar Togo. (Maman Ada)