in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugabannin Togo da Benin za su kai ziyara a birnin Niamey
2015-02-24 17:04:12 cri
Shugaban kasar Benin, Thomas Boni Yayi da na kasar Togo, Faure Eyadema za su kai wata ziyarar aiki a birnin Naimey a ranar yau Talata, a cewar cibiyar watsa labarai ta fadar shugaban kasar Nijar.

Shugabannin kasashen biyu, da ake tsammanin zuwansu a safiyar yau Talata a babban birnin Niamey, za su tattauna tare da takwaransu na kasar Nijar, Issoufou Mahamadou a fadar shugaban kasar a cewar wannan majiya.

Kafin daga baya, shugabannin su shirya wani taron manema labarai domin mai da hankali ga dukkan alamu kan batutuwan huldar dangantaka da tsaro a cikin shiyyarsu musammun ma kan yaki da kungiyar Boko Haram da ke gudanar da ayyukanta na ta'addanci a yankin tafkin Chadi.

Kasashen Benin, Mali da Faransa dai, sun aike a makon da ya gabata da wasu manzanninsu domin kawo goyon baya ga shugaba Mahamadou Issoufou, tare da mika masa wasikun nuna jimami, goyon baya da tallafinsu bayan hare haren da wannan kungiyar ta'addanci ta kai a kasar Nijar. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China