in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bankin BOAD zai zuba kudin sake gina tashar ruwan birnin Lome bisa kudin Sefa biliyan 25
2014-05-10 16:33:30 cri
Bankin ci gaban kasashen yammacin Afrika BOAD zai zuba rabin kudin da suka tashi zuwa Sefa biliyan 25 kwatankwacin dalar Amurka miliyan 50, kan shirin sake gina wuraren ayyuka daman a tashar ruwan birnin Lome, wanda ita ce tasha guda dake cikin ruwan tekun Guinee a wani labarin da ya fito daga cibiyar wannan hukumar kudi dake babban birnin kasar Togo.

Wannan rancen kudi na bankin BOAD ya cimma Sefa biliyan 43 na jimillar adadin ayyukan da bankin yake kan tashar ruwan birnin Lome.

Ayyukan sun shafi sake gina hanyoyi da filayen zirga zirga da suka tsufa a cikin tashar ruwan, gani wani tsarin tsabtacewa, sake gina da fadada tasrin samar da ruwa masu tsabta, gyara tsarin layoyin wutar lantarki da na wayar tarho, fadada manyan hanyoyi, gina wuraren fakin, da gina hanyoyin shiga da fita.

Wadannan ayyuka za su taimaka wa tashar ruwan Lome kara karfin yin takara, kamar irin tashoshin ruwan kasa da kasa, haka kuma zai kara taimkawa wajen harkokin shige da fice daga kasashen Mali, Nijar da Burkina Faso, da ayyukan shige da fice daga wadannan kasashe ya wuce fide kashi 20 cikin 100, in ji shugaban bankin BOAD. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China