in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Togo ya gamsu da aikin kamfannonin Sin na gyara filin jiragen sama na Lome
2013-09-10 15:44:10 cri
Shugaban kasar Togo, Faure Essozimna Gnassingbe ya jagoranci wasu manyan jami'an gwamnati, da babban hafsan hafsoshin rundunar sojin kasar, don ayyukan da kamfannonin kasar Sin ke gudanarwa na gyare gyare a babban filin saukan jiragen sama na Gnassingbe Eyadema dake Lome, inda ya nuna gamsuwar sa sosai kan yadda aikin ke tafiya cikin sauri da kuma ingancinsa.

Ana sa ran za a kashe kudi da yawansu ya kai dalar Amurka miliyan 1500 kan wannan aiki da aka fara gudanar da shi a watan Disamba na shekarar 2011 kudin da aka samu sakamakon shirin samar da rancen kudi mai gatanci daga bankin The Export-Import Bank of China bisa tsarin dandalin tattaunawar hadin kai a tsakanin Sin da kasashen Afrika.

Haka kuma ana sa ran za a kammala aikin a ranar 15 ga watan Agusta na shekara mai zuwa. Bayan kamala aikin filin jiragen sama zai iya yin jigilar fasinjoji daga dubu 400 zuwa dubu 2000 a ko wace shekara, sannan yawan kayayyakin da zai iya jigilar zai karu daga ton dubu 10 zuwa dubu 50 ko wace shekara.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China