in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Manzon musamman na MDD ya yi kira da a gudanar da zaben 'yan majalisar dokokin kasar Togo cikin zaman lafiya
2013-07-25 12:30:39 cri
Babban wakilin sakatare janar na MDD game da yammacin nahiyar Afrika mista Said Djinnit ya yi kira ga jam'iyyun siyasar kasar Togo da su nuna diyauci da sanin ya kamata, ta yadda za a samu damar shirya zaben 'yan majalisar dokoki na ranar 25 ga watan Yuli cikin kwanciyar hankali da zaman lafiya.

Jami'in ya yi wannan furuci ne a lokacin wani taron manema labarai bayan ya kammala wani rangadin aiki na yini daya a ranar Laraba a Lome, babban birnin kasar Togo.

Mista Djinnit ya ce, "ina amfani da wannan dama wajen yin kira ga dukkan masu ruwa da tsaki domin ganin an gudanar da wannan zabe cikin zaman lafiya. Domin zaman lafiya, kwanciyar hankali da tsaro su ne jiga-jigan abubuwan dake da muhimmancin gaske ga ci gaban kasashenmu."

Haka zalika jami'in ya bukaci jam'iyyun siyasa da su yi kokarin kaucewa duk wasu kiraye-kiraye da za su iyar janyo sabani ko tashe-tashen hankali.

Baya ga haka mista Djinnit ya bayyana muhimmancin kawo gyare-gyaren tsarin mulki da na hukumomi, ta yadda kasar Togo za ta tanadi wani tsarin mulki da zai samu amincewar kowa domin tallafawa zaman lafiya da samun ci gaba. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China