in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An fara zaben 'yan majalisar dokoki a kasar Togo
2013-07-26 10:42:44 cri
An fara zaben 'yan majalisar dokoki a kasar Togo ran 25 ga wata da karfe 7 na safe bisa agogon wurin, inda masu jefa kuri'a suka jefa kuri'u a tashoshi sama da dubu 7 da aka kafa a kasar, kuma an gudanar da aikin cikin yanayin lumana.

'Yan takara guda 1174, daga jam'iyyoyi da kungiyoyin siyasa guda 8, da suka hada da kawancen hadin kan jama'ar kasar Togo dake kan gadon mulki da dai sauran jam'iyyu suna fafutukar neman kujeru guda 91 na majalisar dokokin kasa.

Shugaba Faure Essozimna Gnassingbe da kuma firaminista Ahoomey Zunu na kasar Togo sun kada kuri'unsu a wannan rana da safe, kana an kammala jefa kuri'a ran 25 da karfe 4 na yamma.

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasar zata sanar da sakamakon farko na zaben cikin a daren wannan rana. Kungiyar tarayyar kasashen Afirka da kuma gamayyar tattalin arzikin yammacin kasashen Afirka da dai sauran kungiyoyin sun tura masu sa ido kan zaben.

A baya dai an tsai da kudurin gudanar da zaben 'yan majalisar dokokin kasar Togo a watan Oktoba na shekarar 2012, to amma an jinkirtar da hakan saboda bambancin ra'ayi kan harkokin zabe, tsakanin gwamnati da jam'iyyar dake adawa ta kasar. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China