in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Iraqi da dakarun Kurdawa za su yi hadin gwiwa wajen kwato birnin Mosul
2015-04-07 10:18:41 cri
Firaministan kasar Iraqi Haider al-Abadi, ya sanar da cewa, rundunar sojin gwamnatin kasar Iraqi, za ta yi hadin gwiwa da dakarun Kurdawa dake yanki mai cin gashin kansa dake arewacin kasar, domin kwato 'yancin birnin Mosul, da ma sauran yankunan lardin Nineveh da birnin ke ciki, wadanda a halin yanzu, kungiyar IS ta mamaye su.

Mr. Abadi ya bayyana hakan ne a jiya Litinin, lokacin da ya ziyarci Erbil, babban birnin yankin Kurdawa, inda ya yi shawarwari tare da shugaban yankin Massoud Barzani game da hakan.

Bayan kuma kammala shawarwarin nasu, Mr. Abadi ya bayyana wa wani taron manema labaru cewa, gwamnatin kasar Iraqi, da gwamnatin yankin Kurdawa sun kafa wani kwamitin hadin gwiwa, domin gudanar da ayyukan soji a kokarinsu na kwato lardin Nineveh.

Bugu da kari, Abadi ya ce, gwamnatin Iraqi da gwamnatin yankin Kurdawa sun riga sun cimma ra'ayi daya game da jadawalin daukar matakan soja, ko da yake bai yi karin bayani game da jadawalin ba. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China