in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yi maraba da kafa sabuwar gwamnatin Iraqi
2014-09-09 20:07:49 cri
A jiya Litinin 8 ga wata ne, majalisar dokokin kasar Iraqi ta amince da jerin sunayen mambobin majalisar ministoci da Haider al-Abad ya gabatar, kana ta amince da Haider al-Abadi a matsayin firaministan kasar a hukunce.

Dangane da lamarin, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta bayyana cewa, kasar Sin tana maraba sosai da kafa sabuwar gwamnati a kasar Iraqi, wannan wani babban ci gaba ne da aka samu a kokarin da ake yi na warware takaddamar siyasar kasar, kasar Sin na fatan bangarorin kasar Iraqi da abin ya shafa za su ci gaba da karfafa hadin gwiwar a tsakaninsu, don ciyar da yunkurin neman sulhu ta hanyar siyasa da farfado da tattalin arzikin kasar gaba, ta yadda za a iya shimfida zaman lafiya da tsaro a duk fadin kasar cikin sauri, tare da samar da dauwamammen ci gaba a kasar.

Haka kuma, kasar Sin tana son ci gaba da taimakawa kasar Iraqi a lokacin da bukatar hakan taso yadda ya kamata.(Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China