in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Wasu kusoshin kungiyar IS sun rasa rayukansu sakamakon harin sama da kawancen kasa da kasa suka kaddamar
2015-02-27 14:12:38 cri
Wani jami'in hukumar tsaron kasar Iraki ya bayyana jiya Alhamis cewa, dakarun kawancen kasa da kasa wanda Amurka ta jagoranta, ya kai hari ta sama a yankin iyakar yammacin kasar Iraki da kasar Syria, lamarin da ya haddasa mutuwar dakarun kungiyar IS a kalla 15, ciki har da wasu manyan kusoshin kungiyar.

Jami'in ya ce dakarun kawancen kasa da kasan sun samu bayanan sirri, sa'an nan suka kai farmaki ga mayakan da ke garin Al-Qa'im, da maboyar wasu manyan jami'an kungiyar IS, wanda hakan ya haddasa mutuwar dakarun kungiyar IS a kalla 15, tare da jikkata wasu fiye da 30.

Wani jami'in na daban a hukumar tsaron kasar Irakin ya bayyana cewa, sojojin kasarsa za su kaddamar da ayyukan soja a jihar Salahudin dake arewacin kasar cikin awoyi 72 masu zuwa, don murkushe dakarun kungiyar IS dake jihar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China