in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Nijar ya lashi takobin murkushe Boko Haram
2015-02-23 17:24:43 cri
Shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou da ya kai ziyarar aiki a ranar Asabar a jihar Diffa dake kudu maso gabashin kasar mai iyaka da Najeriya, da ta yi fama da hare haren Boko Haram a 'yan kwanakin da suka gabata, ya bayyana imaninsa cewa kasar Nijar zata samu nasara kan yaki da Boko Haram.

Tun a ranar Jumma'a 6 ga watan Febrairu, yankunan Bosso da Diffa na kasar Nijar suka fara fuskantar jerin hare hare daga mayakan kungiyar daga sansanoninsu dake Najeriya, da ma tashe tashen boma bomai daga 'yan ta'addan a birnin Diffa da kewayensa a makwannin da suka gabata.

Hare-haren sun yi sanadiyyar mutuwar mutane kusan 15 a bangaren jami'an tsaro na FDS, a yayin da aka kashe mayakan Boko Haram kusan 280 kana aka cafke wasu kimanin 160.

Yau kusan mako ke nan, zaman lafiya ya dawo a birnin na Diffa tare da taimakon jami'an tsaro na FDS dake sintiri dare da rana.

A lokacin, da yake jawabi ga bangaren jami'an tsaron kasar Nijar da suka shiga yaki da Boko Haram, shugaban kasar Nijar Mahamadou Issoufou yayi alkawarin cewa za su ci nasarar wannan yaki domin a cewarsa, sojojin sun kware wajen yaki kuma sun zabi sana'ar aikin soja, domin su sojoji ne masu juriya da kwazo kana kuna alfahari da aikinku, kuma kuna karkashin ofisoshin da suka nuna kwarewa kan ayyukansu a fagen daga a kasar Nijar da ma ketare.

A yakin da sojojin Nijar suke yi da Boko Haram a kudu maso gabashin Nijar, suna samun taimakon sojojin kasar Chadi, Amurka da kuma sojojin musamman na kasar Faransa. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China