in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
MDD ta yi allah wadai da hare-haren da Boko Haram a kasar Chadi
2015-02-14 17:06:24 cri
Jiya Jumma'a 13 ga wata, kwamitin sulhu na MDD ya fidda wata sanarwa, inda ya yi allah wadai da kakkausar harshe da hare-haren da kungiyar Boko Haram ta yi ta yi, sanarwar ta ambaci harin da kungiyar ta kai kan fararen hula a birnin Ngoubona na kasar Chadi a ran 13 ga wata, da kuma hare-haren da ta kai a kasashen Kamaru da Nijer kwanan baya.

Kwamitin sulhu na MDD ya nuna cewa, dukkanin ire-iren ta'addanci, ciki hada da Boko Haram su kasance daya daga cikin kalubaloli mafi tsanani ga zaman lafiya da tsaro na kasa da kasa.

Haka kuma, kwamitin ya jaddada cewa, yana tsayawa tsayin daka domin yaki da ta'addanci bisa kundin tsarin MDD, ya kuma jaddada cewa, ya kamata a gurfanar da wadanda suka aikata shi, shirya shi ko samar da kudade ga ayyukan ta'addanci gaban kuliya, a sa'i daya kuma, kwamitin ya bukaci kasashen da abin ya shafa su dauki alhakinsu yadda ya kamata bisa dokokin kasa da kasa da kuma kudurorin kwamitin sulhu na MDD da abin ya shafa, da kuma hada kai da bangarori daban daban kan aikin yaki da ta'addanci cikin himma da kwazo. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China