in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An bukaci kasashen Afirka da su sanya hannu kan dokar MLC
2015-02-18 16:35:17 cri
Ministan kwadago da kiyaye tsaron al'umma na kasar Congo Florent Ntsiba ya bukaci kasashen Afirka da su amince da yarjejeniyar harkokin kwadagon da suka shafi teku da aka cimma a shekara 2006.

Ministan ya bayyana hakan ne a yayin da ya ke jawabi a wani taron karawa juna sani kan yadda za a aiwatar da wannan yarjejeniya wanda aka shirya tare da hadin gwiwar kungiyar kwadago ta duniya ILO.

Ya ce, yarjejeniyar za ta taimaka wajen samar da yanayin aikin da ya dace, wurin kwana, nishadantarwa, abinci da kuma yanayin kiwon lafiya mai inganci.

Don haka, ministan ya bukaci kasashe mambobin kungiyar, kungiyar kasashen raya tattalin arzikin tsakiyar Afirka(ECCAS) da su bullo da matakan sa-ido kan 'yancin amfani da iyakokin ruwayensu.

Taron karawa juna sanin na kwanaki hudu ya hallara kan kwararru daga kungiyar ILO da kasashe mambobin ECCAS wadanda suka hada da Jamhuriyar Congo,Gabon,Jamhuriyar Afirka ta tsakiya,Chadi,Kamaru,Equatorial,Guinea,Jamhuriyar demokiradiyar Congo da kuma Angola.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China