in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya za ta yi shawarwarin sulhunta al'ummar ta a karshen shekarar 2014
2014-09-04 20:49:35 cri
Firaministan kasar Afrika ta tsakiya Muhammad Carmon ya ce kasar za ta yi shawarwarin sulhunta al'ummar ta don haka yana fatan jam'iyyu, dakaru da mutane da ba su cikin jam'iyya za su halarci shawarwarin..

Muhammad Carmon ya fadi hakan ne a zantawar sa da manema labaru a kwanan baya inda ya bayyana cewa shawarwari zai baiwa dukkan al'umma wata dama mai kyau wajen daidaita bambancin ra'ayi dake tsakaninsu.

Firaministan wanda lurar da cewa ta haka ne kasar za ta samun farfadowa sai dai bai tabbatar da hakikkanin lokaci da hanyar da za a bi wajen yin shawarwarin ba.

An ce bangarorin biyu dake dauki ba dadi tsakaninsu wato dakarun sojin sa kai na Anti-Balaka da tsohon kungiya mai adawa da gwamnati ta Seleka sun kai ga matsaya daya na dai na zaman gaba a tsakanin su a birnin Brazzaville a ran 23 ga watan Yuli, sakamakon haka ne suka nemi a yi shawarwari tsakanin al'umma.

Bisa wannan yarjejeniyar da suka cimma, shugabar kasar ta wucin gadi Catherine Samba-Panza ta nada Carmon a matsayin sabon firaministan wucin gadi na kasar. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China