in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta Kudu zata gabatar da batun Afrika a taron G20
2014-11-11 17:09:52 cri
Kasar Afrika ta Kudu zata yi amfani da taron G20 dake tafe domin ta gabatarar da batun nahiyar Afrika, a cewar fadar shugaban kasar ta.

Afrika ta Kudu ce kadai kasar Afrika da take cikin kungiyar G20.

Shugaba Jacob Zuma zai jagoranci tawagar kasar sa zuwa taron a birnin Brisbane na kasar Australia daga ranakun 13-16 ga watan nan inji kakakin fadar gwamnati Mac Maharaj.

Shugabannin G20 zasu tattauna tattalin arzikin duniya sakamakon wata farfadowar da ta yi mara karfi.

Traon zai mai da hankali kuma a kan yadda kasashen G20 gaba daya da kowannen su za su dauki Karin mataki domin daga cigaban tattalin arzikin duniya ta fidda tsarin da zai daga GDPn da fiye da kashi 2 cikin 100 a cikin shekaru 5.

Haka kuma ana sa ran Shugabannin BRICS za su gana da junan su a bangaren wannan taron na G20. ganawar zai bada dama ga shugabannin kasashen na BRICS da su waiwaya cigaban da aka samu a kan aiwatar da yarjejeniyar Fortaleza na 2014,musamman ganin ya jibanci sabon bankin cigaba da cibiyarsa a yankin Afrika.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China