in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Afrika ta bayyana fatanta na neman kujerun dindindin biyu a kwamitin sulhu na MDD
2014-05-17 16:19:15 cri
Kungiyar tarayyar Afrika AU ta bukaci da a mika mata kujerun dindindin biyu da wasu biyar da ba na dindindin ba a zauren kwamitin sulhu na MDD bisa kiran da take na kawo gyaran fuska dake fatan ya tabbata.

Wadannan shawarwari na cikin sanarwar karshe ta taron kwamitin kasashe goma na tarayyar Afrika kan batun yi wa MDD gyaran fuska da ya gudana a ranar Jumma'a Oyo, birnin da aka haifi shugaban kasar Congo, Denis Sassou N'Guesso, mai tazarar kilomita 400 daga arewacin birnin Brazzaville.

Dandalin da kasar Congo ta shirya a karkashin shugaban kwamitin, shugaban kasar Sierra-Leone Ernest Bai Koroma tare da taimakon takwarorinsa na kasashen Congo, Guinee-Equatoriale, shugaban kwamitin kasa na Libya, ministocin harkokin wajen kasashe shida da kuma kwamishinonin harkokin siyasa na tarayyar AU.

Makasudin da ake son cimma shi ne Afrika, ta samu 'yancin wakilta a cikin manyan hukumomin gudanarwa na MDD, musamman ma a kwamitin sulhu. Cikin tarihi, Afrika ita ce shiyya kadai a duniya da bata da wakilci a cikin mambobi na dinidindin a kwamitin sulhu na MDD in ji sanarwar karshe ta Oyo. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China