in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban Kasar Kenya ya tashi zuwa kasar Amurka domin halartar wani taron koli
2014-08-04 10:56:48 cri
Shugaban kasar Kenya Uhuru Kenyatta ya tashi jiya Lahadi zuwa Amurka domin halartar wani taron koli da zummar bunkasa huldar yarjejeniyar cinikayya tsakanin kasashen Afirka da Amurka.

Wata sanarwar da aka bayar a Nairobi jim kadan kafin tashin shugaba Kenyatta zuwa Amurka, ta ce shugaban kasar na Kenya zai gana da wasu gungun 'yan kasuwa na kasar Amurka wadanda ke da sha'awar saka jari a kasar ta Kenya.

Wannan taron koli wanda hukumomin kula da cinikayya na kasashen biyu sun shirya shi ne domin jawo hankalin saka jari a kasar Kenya daga kasashen ketare.

Sanarwar ta ce Kenyatta zai halarci taron koli na Amurka da shugabannin kasasshen Africa domin tattaunawa a kan ci gaba mai dorewa da kuma saka jari mai tabbatar da kyakkyawar makomar Africa, zaman lafiya da tsaro.

Wata kididdiga da aka fitar a kasar Kenya a kwanan nan ta nuna cewar cinikayya tsakanin Kenya da Amurka ta kai darajar kudi har fiye da dalar Amurka biliyan daya da miliyan dari 1 a shekarar 2013.

Kasar Kenya na da niyyar kara kaimi wajen neman Amrka ta sabunta yarjejeniya cinikayyar tsakanin Amurka da kasshen Africa na shekaru 15 masu zuwa tare da daddale matsaloli da suka shafi cinikayyar. (Suwaiba)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China