Gwamnatin kasar Senegal ta yanke shawarar sake bude iyakokinta da makwabciyarta Guinea, bayan rufe iyakokin da ta yi a baya, a wani mataki na kare bullar cutar Ebola cikin kasar.
Ma'aikatar harkokin cikin gidan kasar ta Senegal ce ta bayyana hakan cikin wata sanarwa.
Dadin dadawa, sanarwar ta nanata kudurin kasar ta Senegal, na karfafa bincike a tasoshin dake kan iyakokin nata, domin tabbatar da hana shigar cutar Ebola cikin yankunanta. (Amina)