in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An kaddamar da bikin nune-nunen al'adun kasashe masu amfani da harshen Faransanci na shekarar 2014
2014-11-25 11:06:20 cri
A jiya Litinin ne aka kaddamar da bikin nune-nunen al'adu na kasashe masu amfani da harshen Faransanci na shekarar 2014 a dakin wasan kwaikwayo na birnin Dakar dake kasar Senegal, gabanin taron koli na kungiyar kasashen karo na 15 dake tafe.

Ana dai sa ran gudanar wannan biki ne ya zuwa ranar 30 ga watan nan na Nuwamba, inda mahalartansa za su gamewa idanunsu kayayyaki na musamman masu alaka da al'adun kasashe membobin kungiyar kasashe renon Faransa.

Firaministan kasar ta Senegal Mohamed Abdallah Dionne ne dai ya gabatar da jawabin bude bikin nune-nunen. Bikin da aka yiwa lakabi da "yin amfani da fasahohin sadarwa na zamani don sa kaimi ga bunkasa kasa, da al'adun kasashe a fannoni daban daban".

Shi ne kuma kashin da ya shafi nune nunen al'adun gargajiya a taron kolin kungiyar ta kasashe masu amfani da harshen Faransanci na wannan lokaci. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China