in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Za a yi iyakacin kokarin ceto malamin addinin nan da aka yi garkuwa da shi, in ji shugaban Faransa
2013-11-16 16:47:55 cri
A ranar Jumma'a 15 ga wata ne shugaban kasar Faransa François Hollande, ya bayyana cewa an dauke malamin addinin nan dan Faransa da aka yi garkuwa da shi a daren ranar 13 ga wata, a arewacin Kamaru zuwa Nijeriya. Ya mai tabbatar da cewa yanzu haka gwamnatin Faransa na iyakacin kokarin ganin an ceto wannan malami daga hannun wadanda ke tsare da shi.

Shugaba Hollande ya bayyana hakan ne bayan ganawarsa da takwaransa na kasar Togo, Faure Essozimna Gnassingbé a fadar sa dake birnin Faris. Hollande ya bayyana wa kafofin yada labaru cewa, gwamnatin Faransa na kokarin yin binciken sakwannin da aka samu, dongane da wannan malamin addini, zai kuma yi shawarwari da takwaransa na Kamaru kan wannan batu.

Dadin dadawa, shugaba Hollande ya furta cewa, kawo yanzu Faransa tana maida hankali sosai kan batun yaki da ta'addanci. Yace koda yake aikin soja da Faransa ta yi a kasar Mali a bana ya yi babbar nasara, tare da taimakawa gwamnatin Malin wajen maido da cikakken yankin tsaro, duk da haka gwagwarmayar da Faransan ke yi da ta'addanci ba ta kare ba.

Yace ta'addanci na fitowa ta hanyoyi daban daban, kuma ba kasafai ya kan fito ta hanyar da ake tsammani, ko wuri mafi hadari ba.(fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China