in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Faransa za ta shirya wani taron koli game da yaki da 'yan ta'adda
2014-05-14 10:26:22 cri
Bisa bukatun da takwaransa na kasar Najeriya Goodluck Jonathan ya gabatar, shugaban kasar Faransa Francois Hollande zai shirya wani taron koli a ranar 17 ga watan a birnin Paris, don taimaka wa Najeriya da kasashen dake makwabtaka da ita wajen yaki da kungiyoyin 'yan ta'adda. Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Faransa, Romain Nadal ne ya bayyana haka a yayin taron manema labaru da aka shirya a jiya Talata.

Kakakin ya ce, ban da shugabannin kasashen Najeriya, Chadi, Kamaru, Nijer, da kuma Benin, wasu wakilai daga kasashen Amurka, Burtaniya, da kuma kungiyar EU su ma za su halarci taron. Ya kuma kara da cewa, muddin ana fatan murkushe ta'addanci yadda ya kamata, dole ne a kara hadin kai tsakanin shiyya-shiyya da kasa da kasa, ta yadda za a iya musayar bayanai, da sa ido a kan iyakar kasashen juna. Ya kamata kasashen dake shiyyar su dauki babban nauyi wajen yaki da ta'addanci.

Har illa yau kakakin ya bayyana cewa, kasashen Afrika na fatan kara cimma matsaya da Faransa, da kuma samun goyon baya daga kasar da sauran kasashe a fannonin tsare-tsare da fasahohi. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China