in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi garkuwa da wani malamin addini na Faransa a Kamaru
2013-11-15 10:58:20 cri
Ran 14 ga wata, ma'aikatar harkokin wajen kasar Faransa ta ba da wata sanarwa, inda ta nuna cewa, an yi garkuwa da wani malamin addini na kasar a kasar Kamaru.

Sanarwar ta kuma nuna cewa, an yi garkuwa da wannan malami ne a ranar Laraba 13 ga wata da dare a wani yankin arewacin kasar Kamaru dake da nisan kilomita 30 da iyakar kasashen Kamaru da Nijeriya. A halin yanzu, gwamnatin kasar Faransa tana tattaunawa da gwamnatin kasar Kamaru don sanin halin da ake ciki ta yadda za a ceto malamin cikin sauri.

Amma zuwa yanzu, babu wanda ya sanar da daukar alhakin sace malamin.

Yanzu kasar Faransa ta riga ta ayyana yankin arewacin kasar Kamaru a matsayin yanki mai hadari inda ta shawarci 'yan kasarta da kada su je yankin. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China