in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Akalla mutane 12 ne suka rasu a harin da aka kaiwa wani gidan jarida dake birnin Paris
2015-01-07 21:35:34 cri
Ofishin mai gabatar da kara a birnin Paris na kasar Faransa, ya ce wasu mahara sun budewa jama'a wuta, suka kuma hallaka akalla mutane 12, tare da jikkata wasu da dama, a farfajiyar gidan jaridar Charlie Hebdo dake birnin Paris.

Sakamakon harin na Larabar nan, mahukuntan kasar ta Faransa sun tsaurara matakan dakile karin hare-haren ta'addanci a birnin na Paris, musamman ganin cewa 'yan bindigar da suka aikata ta'asar sun tsere.

Yayin ziyarar da ya kai wurin da lamarin ya auku, shugaba Francois Hollande, ya ce ko shakka babu harin ta'addanci ne aka kaddamar, a ofishin da da ma can ya sha fama da barazanar 'yan ta'adda. Matakin da ya sanya a baya aka tsananta tsaro a ofishin.

Shugaba Hollande ya sha alwashin cafke, tare da gurfanar da maharan gaban kuliya. Yana mai cewa kasar sa ta dade da kasancewa wuri, da masu tsauttsauran ra'ayin Islama ke hako, domin kaddamar da harin ramuwar gayya, bisa tallafin da take bayarwa wajen yakin da ake yi da dakarun kungiyoyin 'yan ta'adda a Iraqi, da kuma yankin Sahel na Afirka.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China