in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Firaministan Sin ya gana da shugaban Afirka ta Kudu
2014-12-04 20:14:16 cri
A yau ne firaministan kasar Sin Li Keqiang ya gana da shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma a nan birnin Beijing.

A yayin ganawar, Li Keqiang ya bayyana cewa, kasar Sin tana daukar kasar Afirka ta Kudu a matsayin kasar ketare da ta fi son zuba jari, kuma Sin na sa kaimi da kuma nuna goyon baya ga manyan kamfanonin kirar na'urori na kasarta da sauran kamfanoni masu bunkasa cikin sauri da su je kasar Afirka ta Kudu domin taimakawa wajen ciyar da harkokin masana'antun kasar gaba. Haka kuma, ana son habaka gamayyar moriyar kasar Sin da kasar Afirka ta Kudu, da kuma ciyar da kokarin dunkulewar kasashen Afirka gaba. Bugu da kari, kasar Sin tana son yin hadin gwiwa tare da kasashen Afirka wajen ci gaba da ba da gudumawa kan yaki da cutar Ebola.

A nasa bangare kuma, shugaba Jacob Zuma ya ce, kasarsa na son karfafa shawarwari da hadin gwiwar dake tsakaninta da kasar Sin kan fannonin siyasa, tattalin arziki da cinikayya, albarkatun teku, al'adu da dai sauransu. Kuma kasashen Afirka na maraba da taimakon kasar Sin na samar da kayayyakin more rayuwa, ciyar da yunkurin dunkulewar nahiyar gaba, domin taimaka wa kasashen Afirka wajen cimma burinsu na neman bunkasuwa. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China