in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta nuna yabo ga gwamnatin Afirka ta Kudu wajen goyon bayan ta ga tabbatar da ikon mulkin kasa da cikakken yankin kasar Sin
2014-09-05 20:37:02 cri
A yau Jumma'a 5 ga wata, kakakin ma'aikatar harkokin waje ta Sin mista Qin Gang ya bayyana a gun taron manema labaru cewa, kasar Sin ta yaba ma gwamnatin kasar Afirka ta Kudu bisa ga goyon bayan da ta baiwa ga batutuwan da suka shafi ikon mulkin kasa da cikakken yankin kasar Sin.

Mr Qin ya bayyana hakan ne dangane da matsayin kasar akan tambayar da manema labarai suka mashi kan kin amincewar da gwamnatin Afirka ta Kudu ta yi na hanaga yunkurin neman samun takardar shiga kasar ta gada Dalai Lama ya yi, domin kauracewa mummunan tasiri ga huldar dake tsakaninta da Sin.

Mr Qin ya bayyana cewa, Dalai Lama dan gudun hijira ne dake yunkurin kawo barakahaifar da illa ga cikakken yankin kasa da ikon mulkin kasar Sin da kuma hadin kan al'ummomin kasar ta hanyar amfani da addini, a don haka, Sin bata amince da kokarin Dalai Lama ba wajen kawo mummunan mummunar baraka ga kasar Sin a kasashen waje ta kowace hanya.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China