in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Shugaban kasar Afirka ta Kudu ya gana da ministan tsaron kasar Sin
2014-07-09 10:20:47 cri
Shugaban kasar Afirka ta Kudu Jacob Zuma ya gana a fadarsa da ministan tsaron kasar Sin janar Chang Wanquan dake ziyara a kasar a ran 8 ga wata.

Zuma ya bayyana cewa, kasarsa ta ji dadi da ganin samun babban ci gaba kan ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma daidaito da kuma hadin gwiwar kasashen biyu. Kasar Afirka ta Kudu tana son kara yin mu'amala tare da kasar Sin a fannoni daban daban a MDD da kungiyar BRICS ciki har da fannin tsaron kasa, kana za su yi kokarin bada gudummawa wajen tabbatar da tsaro a nahiyar Afirka har ma a duniya baki daya.

A nasa bangare, janar Chang Wanquan ya ce, kasar Afirka ta Kudu ta kasance mai muhimmaci a nahiyar Afirka har ma da duniya, kasar Sin tana son yin kokari tare da kasar Afirka ta Kudu wajen aiwatar da ayyukan da shugabannin kasashen biyu suka cimma daidaito a kansu, da inganta dangantakar abokantaka a tsakaninsu zuwa wani sabon matsayi, da kara yin hadin gwiwarsu a fannin kiyaye tsaron kasa don bada gudummawa ga jama'arsu da yankuna tare da tabbatar da zaman lafiya da wadata a duniya gaba daya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China