in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kwamitin sulhu na MDD ya kalubalanci Palasdinu da Isra'ila da su dauki matakin sassauta halin da ake ciki
2014-11-20 14:20:01 cri

Kwamitin sulhun MDD ya ba da sanarwa a ran 19 ga wata, inda ya yi kakkausar suka ga harin da aka kaiwa wurin ibadar Yahudawa a birnin Kudus.

Kwamitin ya kuma karawa shugabanni da jama'ar Palasdinu da Isra'ila kwarin gwiwar hada kai da juna, domin sassauta halin da suke ciki, da hana amfani da karfin tuwo, da kaucewa duk wani mataki na takala, da fatan cimma burin wanzar da zaman lafiya cikin hadin gwiwa.

Idan ba a manta ba dai, an kai harin a ranar 18 ga wata ne a wani wurin ibada na Yahudawa, lamarin da ya haifar da rasuwar Yahudawa 4, yayin da kuma 'yan sandan Isra'ila suka harbe wadanda suka kai farmakin su biyu. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China