in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ban Ki-Moon ya yi maraba da cimma yarjejeniyar tsagaita wuta a Gaza
2014-08-11 15:59:26 cri

Babban magatakardan MDD Ban Ki-Moon ya bayyana farin cikinsa game da cimma yarjejeniyar tsawaita dakatar da bude wuta a Gaza, yana mai fatan hakan zai bada damar kaiwa ga cimma yarjejeniya mai dorewa.

Mr.Ban wanda ya bayyana hakan, biyowa bayan amincewar da bangarorin Isra'ila da Falasdinu suka yi, da shawarar dakatar da bude wuta har tsahon sa'o'i 72 sakamakon shiga tsakani da Masar ta yi, ya kuma kara da kira ga dukkanin bangarorin da wannan lamari ya shafa, da su ci gaba da shawarwari da juna, domin kaiwa ga lalubo hanyar kawo karshen rikicin da ya ki ci ya ki cinyewa.

Daga nan sai ya alkawarta goyon bayan MDD, da tallafi ga duk wata manufa ta aiwatar da sulhu, da wanzar da zaman lafiya a yankin na Gaza.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China