in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Congo-Kinshasa ta sanar da kawo karshen cutar Ebola a kasar
2014-11-16 17:40:25 cri
Ministan kiwon lafiya na kasar Congo-Kinshasa Felix Kabange Numbi ya sanar a ran 15 ga wata cewa, an kawo karshen cutar Ebola a kasar.

Ya ce, ya zuwa ranar 15 ga wata, kwanaki 42 sun riga sun wuce ba tare da gano karin mutanen da suka kamu da cutar a kasar ba, lamarin da ya nuna cewa, an kawo karshen cutar Ebola a kasar. Kana, kasar za ta ci gaba da kafa wasu tawagogin agajin gaggawa a cibiyar dake kula da yaduwar cutar Ebola domin fuskanta da sake barkewar cutar a kasar, idan har akwai bukata.

A watan Agusta na shekarar bana, kasar Congo-Kinshasa ta sanar da gano mai dauke da cutar Ebola a lardin Equateur na kasar, a yayin da cutar Ebola take yaduwa da sauri cikin wasu yankunan dake yammacin nahiyar Afirka. (Maryam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China